Home >>
HAUSA FULANI A IDON NA KUSA DA NA NESA
Muhammad Abubakar Zabi

ABSTRACT
Fulani da Hausawa al’umma ce da]]iya wadda ban da Allah ba wanda ya san lokacin ha]uwarsu, sakamakon }arancin kayan rubutu a wancan lokacin. Fulani na cikin }abilu na farko-farko da Hausawa suka fara cu]anya da su. Wannan shi ya kawo bazuwar Fulani ko’ina cikin} asar Hausa. Shi ya sanya wasu makwabtansu na nesa ke yi musu kallon abu guda kawai. Haka kuma shi ya samar musu da sunan Hausa-Fulani sakamakon daddediyar mu’amala wace ta saka suka caku]a da juna, wanda yanzu an kai fagen da Bafulatani ko Bahaushe ba zai iya tantance cewa shi kaza ne, saboda an yi auratayya an kuma gauraya waje guda. Wanda zai yi wuya ka }irga kaka biyu ko uku na zuriyarku baka tarar da wani sirki na Bahaushe ko Bafulatani ba. Ko ta wajen Uwa ko ta wajen Uba. Wannan aikin sai waiwaici asalin Fulani a takaice da na Hausawa da zamatakewa da suturar Fulani da kuma suturar Hausawa. A takaice wannan takarda za taduba yadda ake kallon Hausa Fulani a idon na kusa da na nesa.


Full Text