Home >>
SUNAYEN LAQABI A AL 'ADAR HAUSAWA
Shamsuddeen Isma?ila da Muhammad Abubakar Zabi

ABSTRACT
Hausawa al’umma ce mai riqo da al’ada, wato Hausawa sun rayu a lokacin gargajiya bisa matakan rayuwa har guda uku. Ya fara tun daga haifuwa da aure da kuma mutuwa. A wannan mataki Hausawa sun yi amfani da sunaye iri-iri na gargajiya. Hatta bautarsu a gargajiya suka gudanar da ita a wancan lokaci. Haka kuma sun gudanar da rayuwa bayan karbar addinin Musulunci duk da haka ba su watsar da al’adunsu na gargajiya ba, wajen sanya wa ýaýansu laqabi irin nasu na gargajiya. Kuma sakamakon haduwarsu da Larabawa sun samu tasirin haduwa da su tafuskar Sunaye wanda ya qara samarwa Hausawa sunayen laqabi. A cikin wannan takarda za a dubi sunayen Hausawa lokacin gargajiya tare da sunayen lokaci da sanadi da yanayi da sunayen siffa. Sannan za a duba sunayen Hausawa bayan zuwan musulunci da sunayen asali da sunayen laqabi a al’dar Hausawa. A qarshe, kammalawa za ta biyo baya kafin manazartar takardar da za ta biyo baya.


Full Text